Transcript aminiya

5
AMINIYA
Juma’a, 10 ga Oktoba, 2014
WASIQU
Saqonnin waya
Buhariyya-Aqida
Muna miqa saqon bangajiya
ga ximbin jama‘ar da suka halarci
taron qungiyar magoya bayan
Janar Muhammadu Buhari mai
suna ‘ Buhariyya-Aqida‘. Wadda
aka gudanar a wannan Litinin da
ta gabata, a garin Hadejia da ke
Jihar jigawa. Da fatan kowa ya isa
gidansa lafiya. Allah ya taimaki
janar Baba Buhari, ya ba shi mulkin
Nijeriya.
Daga: Isah Ramin Hudu,
Hadejia. 08060353382.
Ga shugabannin Arewa
Salam Edita barka da aiki
ina so ka ba ni dama inyi kira ga
shugabanin Arewa cewa ya kamata
su tashi tsaye gurin ceto al’ummar
yankin daga wanan hali da muke
ciki a yan zu na rashin tsaro da ci
gaba na yau da kullum da fatan
za su tausaya mana don ci gaban
yankin namu dama qasar baki
xaya. Daga Umar Idirisa Bapps
Askira jihar Borno 07034478412.
Martani ga Muktar Shagari
Maganar da ya yi na cewa,
shugaba Goodluck ya yi ayukan
alheri a yankin Arewa maso
Yamma, inda ya ce, “Goodluck
ya yi aikin Titi a Gusau zuwa
Kontagora,” wannan magana
zuqitamalle ce, don gaskiya kowa
ya san cewa titin Sakwato da na
Shagari da na Tambuwal da na
Aleiro da na Jega da na Koko da na
Yawuri da na Kontagora duk sun
zama tarkon Mutuwa. Don haka
Muktari Shagari da ma munsan
dacewa ‘ba’a mugun sarki, sai
mugun Bafade. Komai nisan jifa
qasa za. Allah ya raka taki gona.
Daga Zaidu Bala Kofa Sabuwa
Birnin Kebbi,
Jihar Kebbin
Najeriya. Gsm 07037697009.
Addu’ar tsari daga zalunci
Edita ka ba ni dama don in
isar da addu’ar neman tsari ga
al’ummar Najeriya. Don haka ma
nike ganinmu karanta Suratul
Munafiqun qafa 10, don Allah ya
kawo mana qarshen zalunci da
makircin munafukan qasar nan.
Daga A.A. U 08151767785.
A kula da direbobi
Aminiya don Allah ina da
fatawa, Wai me yasa gwamnati ba
ta kulawa da direbobi ne? Misali
hanyarmu ta Kaduna zuwa Legas
ba kula da ita, kuma me yasa haka?
Daga Ibrahim 08054517672.
Ga Sarkin Kano
Assalamu alaikum. Don Allah
Edita ka ba ni dama in miqa
saqon taya murnar Babbar sallah
gaMaimartaba Sarkin Kano. Da
fatan ya yi sallah lafiya, tare da
iyalansa. Allah Ya qara wa Sarki
lafiya da nisan kwana. Amin. Daga
Yunusa Hamza 08133183507.
Ga’yan takarar APC
Edita kabana dama in roqi ya
takarar shugabancin qasar nan
a APC ,waxanda suka haxa da
Kwankwaso da Atiku da su haqura
su bar wa Buhari takara. Domin mu
dai a faxin Arewacin Najeriya ba
mu da kamar Janar Muhammadu
Buhari Mai gaskiya. Muna kuma
roqon Gwamna Kwankwaso da
ya tsayar mana da Janar Jafaru Isa
amatsayin xan takarar Gwamnan,
domin shi ma yana da nagartar da
ta fita sauran ’yan takara a jihar
Kano. Muna fatan Allah Ya yi
mana zavi mai amfani. Ya kuma
ba mu basira kada mu yi zaven
tumun dare. Daga Ahmad Tiga
08068643445.
Ga Aminiya
Salamu alaikum. Aminiya da
fatan kun yi sallah lafiya. Allah Ya
maimaita mana. Kuma ya jimamin
makaman da ake shigowa da su don
wargaza Najeriya. To, Allah Ya tsare
mu daga sharrin masu makirci.
Amin. Daga 08126466663.
Ga jama’ar Arewa
Salam. Jama’ar Arewa Musulmi
da Kirista mu haxa kai,mu manta
da bambanicin qabila da na addini.
Don mu gudu tare, mu tsiratare.
Kwankwaso ka sanya mu tagumi
ditan Aminiya, wadda
ta samu karvuwa a
wannan
qasarbaki
xaya, ka ba ni dama in
bayyana takaicina kan yadda
Gwamna Kwankwaso ya sanya
mu tagumi, a tsawon mulkinsa,
tun daga 1999 zuwa 2003,
dakuma dawowarsa a tsakanin
shekarun 2011 zuwa 2014.
Haqiqa rusau xin da aka yi a titin
Ibrahim Taiwo, an cutar da mu,
E
domin gidajen tun a shekarar
1934, Gwamnatin Arewa ta bai
wa Alhaji Alhassan Xantata,
kuma mahaifinmu ya sayi wasu
a hannun xan uwansa, Alhaji
Sanusi Xantata, cikin shekarar
1964. Sannan ’yan KAROTA ma
ba mu daxinsu ba, domin kai da
kanka ka bayyana cewa ba masu
ilimi ka sanya ba. Sannan Mai
girma Gwamna muna zargin
ka rushe masallatai a qalla
401. Akwai al’amura da dama
waxanda idan muka bayyana su
sai a ce adawa ce kawai, amma
haqiqanin gaskiyarmu muke
bayani a kai. Don haka akwai
buqatar ka wanke kanka kafin
wa’adin mulkinka ya qare, ko
kuma, waxanda aka zalunta su
ci gaba neman haqqinsu wajen
Allah. Daga Sabo Muhammad
Ilori, Gida Mai Lamba 64,
Unguwar Gabari.
Allah Ya qara tona asirin masu
shirin wargaza mu. Amin. Daga
08059044449.
yi hawan sallah, amma waccan
sallar da tagabata,wato aramar
sallah, ba ku yi hawa ba. Kun ce
saboda matsalar tsaro. To yanzu
tsaron ya ingant ane. Ku faxi
gaskiyar abin da ya hana ku hawa.
Daga 08117896000.
Ina son ka yi mana cigiyar abokina
Ibrahim Custom, wanda ke zaune
a Sabon gari Zariya. Domin kwana
biyu bamu ji xuriyarsa a Aminiya
ba. Ko ya daina rubutu ne? Daga
08167569141.
Ga Janar Buhari
Aminioya ’yar aman don
Allah ku miqa min saqon “Barka
da Sallah” ga jagoran APC na
qasa, Shugaban asa na 2015, Janar
Muhammadu Buhari, tare da
al’ummar Musulmin duniya baki
xaya. Da fatan an yi sallah lafiya.
Daga Musa Unguwar Mai Yasin,
Xanja, Jihar Katsina 08155648155.
Barkada sallah
Edi Mubarakun ga xaukacin
Musulmin duniya.Kuma muna
addu’a Allah Ya ba mu lafiya da
zaman lafiya. Nagode Edita. Daga
07060799679.
Mu dage da addu’a
Ya ku ’yan uwana talakawa,ba
zargin shugabanni ne mafita ba.
Hakan ma qara kawo mana bala’I
yake yi.. Mu dage da addu’a. Daga
08079156747.
Ga xan sanda mai lambar yabo
Editan Aminiya ina taya xan
sanda kula da ababen hawa”Traffic
Police,”da shugaban qasa ya
karrama da lambar yabo. Daga
08034275846.
Ga Sarakunan gargajiya
Sarakunan gargajiya, na ga kun
Ina Ibrahim Kwastom?
Edita Allah Ya kare mana kai.
Ga Gwamna Wamako
Edita ka bani dama in miqa
saqona ga Gwamna Aliyu
Magatakarda Wamako, Sarkin
Yamma kan alqawarin da ya yi
mana na hanya da gada a Dukamaje.
Daga Alhaji Sani Abubakar Dogon
Daji 08032238844.
Ga Takai xan takarar Gwmnan
Kano
Fatan alheri ga xan takarar
Gwamnan Kano a qarqashin tutar
jam’iyyar PDP, Malam Salihu
Sagir Takai. Da fatan ya yi sallah
lafiya. Allah Ya yi jagora. Daga
08166835313.
AMINIYA
KABIRU A. YUSUF Shugaba kuma Babban Jamiín Gudanarwa
ISIAQ AJIBOLA Manajin Darakta kuma Babban Jamiín Aiwatarwa
MANNIR XAN ALI Daraktan Gudanarwa kuma Babban Edita
MAHMUD JEGA Mataimakin Darakta (Vangaren Labarai)
ALIYU M. AKOSHILE Mataimakin Darakta (Harkokin Kasuwanci)
BALARABE LADAN Muqaddashin Edita
SHEHU O. MOHAMMAD Janar Manaja, Harkokin Gudanarwa
GARBA ALIYU ABUBAKAR Na’ibin Janar Manaja Harkokin Sadarwa
AKEEM MUSTAPHA Manajan Tallace-Tallace
i-mail: [email protected]; Intanet: www.aminiya.com.ng Tes: 08075129644